Daga Unmahani Abdullahi Adakawa
Mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya tabbatar da cewa ba a ga watan Zulqida a jiya lahadi a Nigeria ba.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin harkokin addinin musulunci na fadar Sarkin Musulmi Farfesa Sambo wali Junaidu ya sanyawa hannu kuma aka aikowa manema labarai.

Sanarwar ta ce sakamakon rashin ganin watan a jiya lahadi, watan Shawwal zai cika kwanaki 30 cif-cif.
“Gobe talata 29 ga watan Afirilu it ce za ta zamo 1 ga watan Zulqida na wannan shekara ta 1446.
Da dumi-dumi: Sarki Aminu ya nada sabon Galadiman Kano
Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a ranar asabar ne fadar Sarkin Musulmi ba da umarnin fara duban watan na zulqada.
Haka ita ma kasar Saudiyya ta ba da sanarwar cewa ba a ga watan na Zulqida a fadin kasar ba don haka watan Shawwal zai cika kwanaki 30.