Yadda gwamnan Kano ya ke rabon kujerun aikin hajjin bana kamar gyada

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Al’ummar jihar Kano na cigaba da yabawa gwamnan jihar saboda yadda yake rabon kujerar aikin Hajjin ga rukunonin al’umma.

Kadaura24 ta rawaito tun lokacin Azumin watan Ramadana gwamnan ya rika rabon kujerun ga rukunonin al’ummar da ya rika yin bude baki da su.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Daga cikin rukunonin al’ummar da gwamnan ya rabawa kujerun makkan akwai Kungiyar shugaban ma’aikatu da hukumomin gwamnatin jihar da yan Kannywood da marayu da dai sauransu.

Wannan lamari ya sa wasu daga cikin al’ummar jihar Kano suke yabawa gwamnan bisa wannan aiki da ke yi.

An sulhunta tsakanin Nigeria da Nijar

Wani cikin wadanda aka baiwa kungiyarsu kujerun wanda ya nemi Kadaura24 ta sakaye sunanshi, ya ce ba su taba ganin gwamnan da yake rabon kujerun aikin Hajji kamar gyada ba , tamkar gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf.

A Wannan ranar talata wasu daga cikin Jaruman masana’antar Kannywood suna fitowa a shafikansu na kafafen sada zumunta suna godewa gwamnan bisa yadda ya ba su kujerun aikin hajjin.

Daga cikin wadanda aka baiwa kujerun a Kannywood akwai Marubuciya a masana’antar Fauziyya D Sulaiman da Jarumai irin su Gharzali Miko da TY Shaban da KB International ( Dan gwamna).

InShot 20250309 102403344

Babu shakka daga yadda ake yi musu fatan alkhairi, Kadaura24 ta fahimci mutane da yawa sun yaba da kokarin gwamnan na ganin ya tallafawa al’ummar jihar don su sauke farali a bana.

Rahotanni sun nuna cewa gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf shi ne zai jagoranci tawagar Maniyatan bana da suka fito daga jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...