Gwamna Ganduje ya Mika Sakon ta’aziyya ga Murtala Garo bisa Rasuwar Kanwar Mahaifinsa

Date:

Daga Khadija Abdullahi
 Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya Mika Sakon ta’aziyyarsa ga kwamishinan kananan hukumomi da masarautu, Murtala Sule Garo bisa rasuwar kanwar Mahaifinsa Hajiya Hadiza Galadima Abubakar.
Cikin Wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran Gwamnan Malam Abba Anwar ya aikowa Kadaura24 yace Rashin Hajiya Hadizan Babban rashi ne ga al’ummar Jihar Kano.
 Gwamna Ganduje ya bayyana cewa “Don haka ina mika wannan ta’aziyya ga kwamishinan kananan hukumomi da masarautu, Murtala Sule Garo, da daukacin iyalanta, da al’ummar garin Garo da karamar hukumar Kabo, a madadin gwamnati da al’ummar jihar Kano.
 Ya kuma addu’ar Allah ya gafarta, Sannan ya bukaci ‘yan uwa da su Kara Hakurin rashinta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...