Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kaduna ta dage dokar dakatar da hanyoyin sadarwa a Jihar

Date:

Daga Abdulmajid Habib Isa Tukuntawa
 Gwamnatin jihar Kaduna ta dage dakatarwar da ta yiwa Hanyoyin sadarwa Wanda aka dakatar na tsawon watanni uku sakamakon hare-haren da ‘yan bindiga suke kaiwa Wasu sassan Jihar Kaduna.
 Gwamnatin jihar ta bakin kwamishinan tsaron cikin gida da harkokin cikin gida Samuel Aruwan, wanda ya sanar da hakan a ranar Juma’a, ya ce an umarci hukumar da ta dace da harkokin sadarwa da ta dage dakatarwa.
Daily Trust ta ruwaito cewa, Saboda bukatar hukumomin tsaro gwamnatin jihar ta umurci hukumar sadarwa ta kasa (NCC) da ta rufe harkokin sadarwa a wasu kananan hukumomin jihar.
 Sai dai Rahotanni sun ruwaito cewa an samu karuwar ‘yan fashi da makami musamman a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja a lokacin da aka dakatar da hanyoyin sadarwar.
 Aruwan ya ce sauran matakai kamar dokar hana babura, hana kasuwannin mako-mako, sayar da man fetur a cikin jarakuna na ci gaba da aiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...