Gwamna Ganduje ya Mika Sakon ta’aziyya ga Murtala Garo bisa Rasuwar Kanwar Mahaifinsa

Date:

Daga Khadija Abdullahi
 Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya Mika Sakon ta’aziyyarsa ga kwamishinan kananan hukumomi da masarautu, Murtala Sule Garo bisa rasuwar kanwar Mahaifinsa Hajiya Hadiza Galadima Abubakar.
Cikin Wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran Gwamnan Malam Abba Anwar ya aikowa Kadaura24 yace Rashin Hajiya Hadizan Babban rashi ne ga al’ummar Jihar Kano.
 Gwamna Ganduje ya bayyana cewa “Don haka ina mika wannan ta’aziyya ga kwamishinan kananan hukumomi da masarautu, Murtala Sule Garo, da daukacin iyalanta, da al’ummar garin Garo da karamar hukumar Kabo, a madadin gwamnati da al’ummar jihar Kano.
 Ya kuma addu’ar Allah ya gafarta, Sannan ya bukaci ‘yan uwa da su Kara Hakurin rashinta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...