Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Gidaje

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu
 Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya jagoranci rantsar da Sabon kwamishinan gidaje Ibrahim Yakubu Adamu .
 A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24, ya ce Kwamishinan shari’a na jihar Kano, Haruna Isah Dederi ya takabawa ba sabon kwamishinan a ranar Litinin.
InShot 20250309 102403344
Talla
 Kafin nadin nasa, Adamu shi ne Manajan Darakta na Hukumar Tsara burane ta Kano (KNUPDA).
 Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Yusuf ya yaba da kwarewar sabon kwamishinan da irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban Kano.
 Ya bayyana muhimmiyar rawar da Adamu ya taka wajen tsarawa da raya garuruwan Kwankwasiyya, Amana, da Bandirawo tsakanin 2013 zuwa 2015 a karkashin gwamnatin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.
 Gwamnan ya yaba da rawar da Adamu ya taka a matsayin Kwamishinan Ayyuka da Gidaje daga 2011 zuwa 2015, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen aiwatar da manyan ayyukan gidaje.
 Gwamna Yusuf ya kalubalanci sabon kwamishinan da ya tabbatar ya magance matsalolin gidaje a Kano, musamman wadanda suka shafi ma’aikatan gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...