Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Gidaje

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu
 Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya jagoranci rantsar da Sabon kwamishinan gidaje Ibrahim Yakubu Adamu .
 A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24, ya ce Kwamishinan shari’a na jihar Kano, Haruna Isah Dederi ya takabawa ba sabon kwamishinan a ranar Litinin.
InShot 20250309 102403344
Talla
 Kafin nadin nasa, Adamu shi ne Manajan Darakta na Hukumar Tsara burane ta Kano (KNUPDA).
 Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Yusuf ya yaba da kwarewar sabon kwamishinan da irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban Kano.
 Ya bayyana muhimmiyar rawar da Adamu ya taka wajen tsarawa da raya garuruwan Kwankwasiyya, Amana, da Bandirawo tsakanin 2013 zuwa 2015 a karkashin gwamnatin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.
 Gwamnan ya yaba da rawar da Adamu ya taka a matsayin Kwamishinan Ayyuka da Gidaje daga 2011 zuwa 2015, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen aiwatar da manyan ayyukan gidaje.
 Gwamna Yusuf ya kalubalanci sabon kwamishinan da ya tabbatar ya magance matsalolin gidaje a Kano, musamman wadanda suka shafi ma’aikatan gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...