Zaben 2027: Kwankwaso ya bugi kirji

Date:

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano, ya ce jam’iyyar NNPP za ta kayar da dukkan jam’iyyun siyasa a zabe mai inganci da adalci.

Kwankwaso ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) na jam’iyyar a Abuja.

InShot 20250115 195118875
Talla

Dan takarar NNPP a zaben 2023 din ya soki gwamnatin Bola Tinubu, yana mai cewa ‘yan Najeriya na fuskantar matsin rayuwa fiye da yadda aka taba gani a baya.

“Gaskiya ne da wuya a tuna da wani da ke farin ciki da gwamnatin APC a kowane mataki, musamman a matakin tarayya,” in ji shi.

“‘Yan Najeriya sun shaida wahalhalu da ba a taba gani ba a tarihin wannan kasa.

Dan Majalisar NNPP ya fice daga jam’iyyar zuwa APC

“Talauci ya yadu ko’ina. Mun ga rashin tsaro, gine-gine da ababen more rayuwa suna lalacewa, kuma ba mu ga wani kokari na gyara su ba.

“Na yi imani idan aka gudanar da sahihin zabe a wannan kasa, jam’iyyarmu za ta kayar da APC, PDP da sauran jam’iyyu.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Inganta ilimi: Jaridar New Telegraph ta Karrama Gwamnan Kano

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Sanarwa ta musamman ga masu neman shiga aikin dansanda

Hukumar kula da aikin 'yan sanda na Kasa (POLICE SERVICE...

Za mu kashe Sama da Naira miliyan 105. Dan Bunkasa Harkar ilimi a karamar hukumar Dala – Hon Surajo Imam

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Surajo...

Sha’aban Sharada ya sami sabon mukami

Daga Sharifiya Abubakar   Kungiyar ‘yan majalisun dake kula da tsaro...