Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Date:

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da bincike na musamman dan gano musabbabin rikicin da ya faru a unguwar Rimin zakara wanda yai sanadiyyar rasa rayukan mutane.

Kwamishinan yada labarai na jihar Kano Kwamred Ibrahim Abdullahi Waiya ne ya bayyana hakan a zantawarsa da manema labarai kan rikicin da aka samu tsakanin jami’an tsaro da mutanan dake zaune a yankin.

InShot 20250115 195118875
Talla

Waiya ya kuma ce Jami’ar Bayero ce ta nemi taimakon gwamnatin Kano dan a dawo mata da filayenta, wanda hakan yasa ta shiga tsakani kuma aka baiwa mutanan dake zaune a gurin wa’adin tashi kasancewar lokacin da aka basu ya riga ya kare.

Daga nan waiya yace bata gari ne suka shiga cikin lamarin Domin tada zaune tsaye duk kuwa da jami’an tsaron da Wadancen Mutanen suka gayyato gudun tada fitina.

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Kwamishinan yada labarai da ayyukan cikin gida Kwamred Ibrahim Abdullahi Waiya yace, lallai Gwamnatin Kano zata kafa kwamitin da zai gudanar da bincike Kan Wanda suka haddasa rikicin da yayi sanadiyyar rayukan Mutane uku.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito al’ummar unguwar Rimin zakara a jiya litinin sun zargi ma’aikatar Kasa ta Kano da rushe musu gidajensu da hadin kan jami’ar Bayero, lamarin da ya jawo har jami’an tsaro suka kashe mutane 4 tare da jikka wasu 16 .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...