Sulhunta Kwankwaso da Ganduje zai amfanar da Kano da Kanawa – Musa Iliyasu Kwankwaso

Date:

 

 

Babban Daraktan kudi na hukumar raya kogunan Hadeja-Jama’are Musa Iliyasu Kwankwaso ya ce yana goyon bayan a sami sulhu tsakanin tsofaffin gwamnonin jihar Kano Kwankwaso, Ganduje, Shekarau da Kabiru Gaya.

” Tabbas sulhunta wadannan mutane zai taimakawa jihar Kano ta sami cigaba, wanda duk al’ummar jihar za su yi alfahari da shi, don haka sulhuntasu abu ne mai kyau”.

Musa Iliyasu Kwankwaso ya bayyana hakan yayin wata ganawa da yayi da jaridar Kadaura24 ranar laraba.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya ce akwai takaici yadda ake mayar da Kano baya ta hanyar soke wani abun alkhairi da daya daga cikinsu ya yiwa jihar Kano komi yadda al’umma suke amfana da aikin.

Zargin cin zarafi: Ƴansanda sun kama hadimin Gwamnan Kano

” So muke tsofaffin gwamnonin su rika hada kansu wajen daukar wasu matakai da zasu inganta rayuwar al’umma, sannan su amince a junansu cewa duk wanda ya sanya hannu akan wani aiki da zai amfanar da al’umma Kar wani ya zo saboda sabanin Siyasa a soke aiki”.

Ya ce dukkanin tsofaffin gwamnoni sun haura shekaru 65 don haka lokaci ya yi da ya kamata su hada hannu waje guda don ciyar da jihar Kano gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...