Daga Sidiya Abubakar
Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON a karkashin jagorancin shugabanta Farfesa Abdullahi Saleh Usman ta sanar da kudin tafiya aikin hajjin bana, an dai sanar da kudin ne bayan amincewar ofishin mataimakin shugaban kasar tarayyar Najeriya.
Hakika Shugaban Hukumar NAHCON da tawagarsa tare da hadin gwiwar wakilin fadar shugaban kasa, Malam Ameen Amshi, wanda shi ne mataimaki na musamman ga shugaban kasa, ayyuka na musamman sun yi iyakacin kokarinsu wajen ganin an fitar da kudin aikin Hajji daidai da yadda aka biya a baya.
A sanarwar da mataimakiyar daraktar yada labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace an cimma wannan matsayar ne bayan tattaunawa mai zurfi don tabbatar da an saukakawa maniyatan Nigeria.

An dai kayyade kudin aikin hajjin ne la’akari da bisa da kuma shiyyoyin kasar kamar haka:
shiyyar Borno da Adamawa, ana sa ran maniyyata za su biya Naira miliyan 8,327,125.59 ( miliyan takwas da dubu dari uku da ashirin da bakwai, da dari da ashirin da biyar da Naira hamsin da tara kobo).
Maniyyatan da Suka fito daga jihohin Kudancin Nigeria kuma za su biya Naira 8, 784, 085.59 (miliyan takwas, da dubu dari bakwai da tamanin da hudu, Naira tamanin da biyar Naira kobo hamsin da tara).
Maniyyatan da suka fito daga shiyyar Arewa za su biya Naira miliyan 8, 457,685.59 ( miliyan takwas da dubu dari hudu da hamsin da bakwai, da dari shida da tamanin da biyar Naira hamsin da tara kobo).
Farfesa Saleh ya yabawa daukacin tawagar inda ya bayyana cewa an fitar da kudin aikin Hajjin da hadin gwiwa da duk masu ruwa da tsaki.