Gwamnan Yusuf ya ja kunnen sabbin kwamishinonin Kano

Date:

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ba da tabbacin ɗaukar matakin daya dace akan duk kwamishinan da ya yi wasa da aikin da gwamnati ta dora masa.

” A wannan lokaci da muke ciki ba za mu lamunci dukkan wani sakaci daga wani kwamishina ba, dan haka dukkan kwamishinan da ya kawo wasa za mu ɗauki matakin da ya kamata akan shi” .

Kadaura24 ta rawaito Alhaji Abba Kabir ya bayyana haka ne a yayin zaman majalisar zartarwa karo na 23 da aka gudanar a gidan gwamnati.

Talla

Gwamna Yusuf ya kuma ja hankalin sababbin kwamishinoni da ya nada da su haɗa kai da sauran kwamishinoni dare da aiki guri guda domin ciyar da jihar Kano gaba

Yayin zaman majalisar zartarwar gwamna Abba Kabir ya kuma bayyana wasu shirye-shiryen da gwamnatinsa za ta gabatar nan bada jimawa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...