Zan Fito da Sabbin tsare-tsare domin ciyar da Ilimi gaba a Kano – Dr. Ali Haruna Makoda

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Sabon kwamishinan Ilimi na jihar kano Dr. Ali Haruna Makoda ya kama aiki a hukumance, inda ya yi alkawarin kara bullo da wasu shirye-shirye da nufin bunkasa fannin ilimi a jihar.

Da yake jawabi ga ma’aikata, yan uwa da abokan arzikin da suka yi masa rakiya, Dr. Makoda ya amince da dimbin tsare-tsare da gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta bullo da su tare da bayyana aniyarsa ta ciyar da su gaba.

Ya kuma jaddada bukatar yin aiki tukuru da jajircewa domin ganin ma’aikatar ta samu ci gaba.

Talla

Sabon Kwamishinan ya baiwa ma’aikatan tabbacin ci gaba da fadada shirye-shirye masu kyau da tsohon kwamishinan ma’aikatar ya bullo da su.

Dr. Ali Makoda ya bukaci ma’aikatan da su kasance masu ba da gudunmawa wajen aiwatar da manufofi da tsare-tsare da gwamnati mai ci ta bullo da su domin amfanin jama’a da jihar.

Gwamna Kano ya kara mutum 1 cikin kwamishinonin da Majalisa ta tantance

Kwamishina mai barin gado Alhaji Umar Haruna Doguwa ya nuna jin dadinsa da samun damar yin aiki a ma’aikatar tare da bayyana wasu nasarorin da aka samu a zamaninsa.

Nasarorin sun haɗa da: Ƙara yawan kasafin kuɗin da ake warewa fannin ilimi, Inda aka ware 30% a cikin 100 a Shekarar 2024 da 31% a Shekarar 2025.

“Gwamnatin gyaran makarantu a fadin kananan hukumomi 44

– Gina ajujuwa da ƙera kayan ɗalibi mai kujeru 3.

“Samar da kayan aiki a makarantu da inganta tsarin ciyarwa a makarantu

Babban sakataren ma’aikatar ilimi, Alhaji Bashir Baffa Muhammad, ya yi addu’ar Allah ya baiwa kwamishinonin biyu ikon yi musu jagoranci a sabbin ayyukan da aka ba su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...