Gwamna Kano ya kara mutum 1 cikin kwamishinonin da Majalisa ta tantance

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

Majalisar dokokin jihar Kano,ta tabbatar da sunayen mutane bakwai da Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya aike mata domin tantance don ya nada su a matsayin kwamishinoni kuma mambobin majalisar zartarwa ta jihar.

Kafin tabbatar da su, sai da mutanen bakwai suka kwace sama da sa’o’i uku da rabi, inda majalisar ta amincewa gwamnan ya nada su a matsayin kwamishinoni.

Talla

Kakakin majalisar Rt. Hon. Jibril Ismail Falgore, ya bayyana cewa gwamnan ya sake aiko da Sunan Nura Iro Ma’aji domin tantance shi a matsayin kwamishina bayan wadancan sunaye na Mutane shida da aka fara tura sunayensu.

Ga sunayen wadanda Majalisar ta Amince da su:

Tsohon shugaban ma’aikata: Shehu Wada Sagaji, wanda aka sauke shi daga mukaminsa a ranar Alhamis din da ta gabata.

Kotun Ƙoli ta kori ƙarar da ke neman ta sauke Tinubu daga shuagaban Nigeria

1. Ambassador Ibrahim Waiya

2. Shehu Wada Sagagi

3. Abdulkadir Abdulsalam

4. Gaddafi Sani Shehu

5. Dr. Dahiru Hashim Muhammad

6. Dr. Ismail Aliyu Dannaraya

7. Nura Iro Ma’aji

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...