Gwamna Namadi ya janye dakatarwar da ya yi wa Kwamishinansa bayan kotu ta wanke shi

Date:

Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya dage dakatarwar da aka yi wa Kwamishinan ayyuka na Musamman, Auwalu Dalladi Sankara, daga yanzu nan take.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ya sanyawa hannu.

Talla

“Za a iya tunawa cewa an dakatar da kwamishinan bisa zargin da ake yi masa kan faruwar wani al’amari daga rahotan hukumar Hisbah ta jihar Kano”, inji Sakataren Gwamnatin.

Ce-ce ku-ce ta barke bayan da mataimakin shugaban kasa ya ambaci Sarki Sanusi II a matsayin Sarkin kano

Sanarwar ta ce an dage dakatarwar ne bayan kotu ta wanke Kwamishinan.

Idan za’a iya tunawa an dakatar da Kwamishinan ne sakamakon zarginsa da mu’amala da matar aure, lamarin da ya kai ga kaisu Kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...