Gwamna Namadi ya janye dakatarwar da ya yi wa Kwamishinansa bayan kotu ta wanke shi

Date:

Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya dage dakatarwar da aka yi wa Kwamishinan ayyuka na Musamman, Auwalu Dalladi Sankara, daga yanzu nan take.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ya sanyawa hannu.

Talla

“Za a iya tunawa cewa an dakatar da kwamishinan bisa zargin da ake yi masa kan faruwar wani al’amari daga rahotan hukumar Hisbah ta jihar Kano”, inji Sakataren Gwamnatin.

Ce-ce ku-ce ta barke bayan da mataimakin shugaban kasa ya ambaci Sarki Sanusi II a matsayin Sarkin kano

Sanarwar ta ce an dage dakatarwar ne bayan kotu ta wanke Kwamishinan.

Idan za’a iya tunawa an dakatar da Kwamishinan ne sakamakon zarginsa da mu’amala da matar aure, lamarin da ya kai ga kaisu Kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...