Gwamnan Kano zai sauya wasu daga cikin kwamishinoninsa

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba zai cire wasu mambobin majalisar zartarwa da aka tantance kwazonsu a ƙarƙashin abin da aka tsara su yi.

Gwamna Yusuf, wanda ya tabbatar da karɓar rahoton kwamitin duba aikin mambobin majalisar, ya bayyana cewa jama’a za su ji matakin da gwamnati za ta ɗauka nan ba da jimawa ba.

Talla

Mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin-Tofa ne ya bayyana haka a ciki wata sanarwa da ya aikowa kadaura24.

Gwamnan ya tunatar da al’umma game da shirin sauya wasu daga cikin mambobin majalisar a wata hira kai-tsaye da aka yi da shi ta gidan rediyo tare da wasu kafofin yada labarai da aka gudanar a Fadar Gwamnati a ranar Laraba.

Gwamnan Kano ya gabatarwa majalisar dokoki kasafin kudin 2025

Ya bayyana cewa rahoton ba zai yi amfani yanzu ba, saboda kasancewarsa tare da su a tsawon shekara ɗaya da rabi ya ba shi damar sanin ƙwarewar su sosai, don haka zai yanke hukuncin karshe game da su da kansa.

Ya bayyana cewa babu ɗaya daga cikin kwamishinonin da suka riƙa neman mukamin, yana mai jaddada cewa kafin naɗin su, ya yi la’akari da ƙwarewa, amana, da kuma shawara daga masu bada shawara.

Ya ce abin da nake buƙata daga kwamishinoni shi ne su kasance masu biyayya gare ni, ga jam’iyyar NNPP, da kuma Tafiyar Kwankwasiyya, tare da jajircewa a kan aikin su da kuma kawo sabbin dabaru don cigaban jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...