Gwamnan Kano zai sauya wasu daga cikin kwamishinoninsa

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba zai cire wasu mambobin majalisar zartarwa da aka tantance kwazonsu a ƙarƙashin abin da aka tsara su yi.

Gwamna Yusuf, wanda ya tabbatar da karɓar rahoton kwamitin duba aikin mambobin majalisar, ya bayyana cewa jama’a za su ji matakin da gwamnati za ta ɗauka nan ba da jimawa ba.

Talla

Mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin-Tofa ne ya bayyana haka a ciki wata sanarwa da ya aikowa kadaura24.

Gwamnan ya tunatar da al’umma game da shirin sauya wasu daga cikin mambobin majalisar a wata hira kai-tsaye da aka yi da shi ta gidan rediyo tare da wasu kafofin yada labarai da aka gudanar a Fadar Gwamnati a ranar Laraba.

Gwamnan Kano ya gabatarwa majalisar dokoki kasafin kudin 2025

Ya bayyana cewa rahoton ba zai yi amfani yanzu ba, saboda kasancewarsa tare da su a tsawon shekara ɗaya da rabi ya ba shi damar sanin ƙwarewar su sosai, don haka zai yanke hukuncin karshe game da su da kansa.

Ya bayyana cewa babu ɗaya daga cikin kwamishinonin da suka riƙa neman mukamin, yana mai jaddada cewa kafin naɗin su, ya yi la’akari da ƙwarewa, amana, da kuma shawara daga masu bada shawara.

Ya ce abin da nake buƙata daga kwamishinoni shi ne su kasance masu biyayya gare ni, ga jam’iyyar NNPP, da kuma Tafiyar Kwankwasiyya, tare da jajircewa a kan aikin su da kuma kawo sabbin dabaru don cigaban jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...