Zargin cin zarafi: Likitoci sun janye yajin aikin da suka Fara, bayan ganawa da gwamnan Kano

Date:

 

Kungiyar Likitoci ta kasa reshen jihar jihar Kano ta janye yajin aikin da suka fara a daren jiya, bayan Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusif ya sami nasarar sasanta rikicin dake faruwa, tsakanin kungiyar da kuma Kwamishiniyar Ma’aikatar Jin-kai ta jihar.

Shugaban Kungiyar Likitoci na jihar Kano Dakta Abdurrahman ne ya tabbatar da hakan, a yayin zantawar sa da manema Labaran a fadar Gwamnatin Kano.

Talla

Sanarwar da Kakakin Gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aiko wa jaridar kadaura24 ta ce yanzu haka likitocin sun koma bakin aiki domin ci-gaba da baiwa marasa lafiya cikakkiyar kulawar da suka saba.

Dakta Abdurrahman ya ce sun janye yajin aikin ne bayan wani zama na musamman da Gwamnan Kano, akan sabanin da aka samu a tsakanin Mambarsu da kuma Kwamishiniyar Ma’aikatar jin kai ta jihar kano.

Ku janye yajin aiki, zan hukunta duk wanda aka samu da laifi – Gwamnan Kano ga Likitoci

Ya kuma yaba wa Gwamnan a bisa gaggawar daukar matakin da ya kamata akan lamarin, harma yayi kira ga al’ummar jihar da su dinga bin dukkan hanyoyin da suka dace wajen shigar da korafin su akan jami’an lafiya domin a sami damar yin adalci ta hanyar bincika wa dama daukar matakin da ya kamata.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito an sami rashin jituwa tsakanin kwamishiniyar da wata likita wanda hakan yasa wasu daga cikin al’ummar jihar Kano sun goyi bayan kiran da Kungiyar likitocin ta yi na gwamnan Kano ya sauke kwamishiniyar daga mukaminta domin tana amfani da shi wajen cin zarafin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...