Dalilin da ya sa yan Najeriya suka kwana cikin duhu ranar Litinin

Date:

 

 

Najeriya ta sake fuskantar katsewar wutar lantarki sakamakon lalacewar babban layin lantarki na ƙasar a ranar Litinin.

Layin ya lalace ne da misalin ƙarfe 7 na yamma, kamar yadda sanarwa daga kamfanin rarraba lantarki ta ƙasa (TCN) ya bayyana.

Talla

Lamarin ya jefa miliyoyin ‘yan ƙasar da kuma sana’o’insu cikin duhu.

Wannan dai shi ne karo na biyar da layin ke lalacewa a shekarar 2024.

Abba tsaya da kafarka: Sakataren gwamnatin Kano Baffa Bichi ya Magantu

Shi ma kamfanin rarraba hasken wutar lantarki reshen jihar Kano (KEDCO) ya nemi afuwar kwastomominsa kan abin da ya faru a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X.

“Muna bakin cikin sanar da ku cewa an samu ɗaukewar wuta ne sakamakon matsalar da aka samu a layin wuta na ƙasa,” kamar yadda shugaban sashen sadarwa na kamfanin Sani Bala ya bayyana.

Ya ce hakan ne ya janyo rashin rarraba wutar zuwa ga kwastomomi.

“Muna rokon al’umma da su yi hakuri yayin da muke ci gaba da aiki tukuru don shawo kan matsalar ta faru da kuma mayar da wutar lantarki yadda muka saba,” in ji shi.

Talla

Ya buƙaci mutane da su kula sosai wajen kare kai daga masu sata ko lalata wayoyin wutar lantarki.

Mene ne babban layin wutar lantarki na Najeriya kuma yaya yake aiki?

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kisan ɗalibai a Kano: Kwamitin Malamai da Iyayen yara na jihar ya nuna damuwarsa

Daga Abdulhamid Isah D/Z Malam Salisu Abdullahi shugaban kwamitin malamai...

Hakikanin halin da gwamnan Katsina yake ciki, bayan wani hatsari

  Rahotanni daga Katsina na cewa gwamnan jihar Katsina Dikko...

Zargin almundahana: ICPC ku fita daga harkokin Siyasar Kano – Kungiyar Ma’aikatan KANSIEC

Daga Hafsat Abdullahi Darmanawa   Kungiyar ma'akatan wucin gadi da suka...

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...