Karin Farashin Mai: Atiku ya yiwa Tinubu wankin babban bargo

Date:

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya caccaki shugaban Najeriya, Bola Tinubu kan abin da ya kira gazawarsa wajen tafiyar da sha’anin makamashi.

Atiku Abubakar wanda ya yi takara da Tinubu a zaɓen 2023, ya wallafa a shafinsa na X a ranar Alhamis cewa gwamnatin Tinubu ta lalata al’amura da sunan cire tallafin mai.

Talla

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar, ya danganta matsalolin da ƴan Najeriya ke fuskanta da irin tsarin gwamnatin Tinubu na “ta ci barkatai” kan yadda take tafiyar da sha’anin makamashi.

Matsin rayuwa: Ana zaluntarku kun kasa komai, Amaechi ga yan Nigeria

Atiku ya kuma bayyana damuwa kan ƙamarin da hauhawar farashi ya yi a ƙasar inda ya ce al’amarin da matuƙar ƙuntata wa ƴan Najeriya.

“Riƙon sakainar kashi da wannan gwamnatin ke yi wa tsarin cire tallafin mai shi ne babban dalilin da ya sa muke cikin yanayin ƙunci da muke ciki a ƙasar nan.

Talla

“A yanzu haka, babu wani fata dangane da hauhawar farashin kaya wanda ya karya ƙarfin tattalin arziƙin ƴan Najeriya.

“Abin takaici ma shi ne yadda al’amarin ba ya damun T-pain,” Kamar yadda Atiku ya rubuta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...