Karin Farashin Mai: Atiku ya yiwa Tinubu wankin babban bargo

Date:

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya caccaki shugaban Najeriya, Bola Tinubu kan abin da ya kira gazawarsa wajen tafiyar da sha’anin makamashi.

Atiku Abubakar wanda ya yi takara da Tinubu a zaɓen 2023, ya wallafa a shafinsa na X a ranar Alhamis cewa gwamnatin Tinubu ta lalata al’amura da sunan cire tallafin mai.

Talla

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar, ya danganta matsalolin da ƴan Najeriya ke fuskanta da irin tsarin gwamnatin Tinubu na “ta ci barkatai” kan yadda take tafiyar da sha’anin makamashi.

Matsin rayuwa: Ana zaluntarku kun kasa komai, Amaechi ga yan Nigeria

Atiku ya kuma bayyana damuwa kan ƙamarin da hauhawar farashi ya yi a ƙasar inda ya ce al’amarin da matuƙar ƙuntata wa ƴan Najeriya.

“Riƙon sakainar kashi da wannan gwamnatin ke yi wa tsarin cire tallafin mai shi ne babban dalilin da ya sa muke cikin yanayin ƙunci da muke ciki a ƙasar nan.

Talla

“A yanzu haka, babu wani fata dangane da hauhawar farashin kaya wanda ya karya ƙarfin tattalin arziƙin ƴan Najeriya.

“Abin takaici ma shi ne yadda al’amarin ba ya damun T-pain,” Kamar yadda Atiku ya rubuta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...