Matsin rayuwa: ‘Ana zaluntarku kun kasa komai, Amaechi ga yan Nigeria

Date:

 

 

 

Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya bayyana rashin jin dadinsa da yadda ƴan Nijeriya su ka zauna suna kallo an jefa su cikin mawuyacin hali na tattalin arziki.

Talla

Da ya ke magana a wata hira da gidan talabijin na ABN TV, Amaechi ya yi tambaya kan dalilin da ya sa ‘yan Najeriya ba sa kwarmata halin wuya da su ke ciki, yana mai nuni da hauhawar farashin kayayyaki da kuma rashin iya biyan bukatun yau da kullum kamar man fetur.

Yanzu-yanzu : NNPC ya kara kudin litar mai a Nijeriya

Tsohon gwamnan na Rivers ya ce shi kan sa ba zai iya siyan dizal ba.

Amaechi ya ce yana sa ran matasa za su mamaye tituna daban-daban su yi zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa.

Talla

Ya ce: “Ina fushi da ’yan kasa. Na sha fadi hakan. Za ka ga gungun mutane suna sace maku kudi suna talauta ku, ba za ku iya siyan mai da komai ba.

“Ya kamata mutane su yi fushi. Kamata ya yi a yi zanga-zanga. Ba ma zanga-zangar adawa da kowa ba sai ga ’yan siyasa. A rika cewa ‘ba za mu zabe kuba” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...