Yan Sumoga ne ke Jawo Tashin Farashin Shinkafa a Niigeria – Ministar Kudi

Date:

Daga Maryam Adamu Mustapha

Ministar Kuɗi ta Najeriya Zainab Ahmed ta ce masu fasa ƙwauri ko kuma sumoga ne ke jawo tashin farashin shinkafa a kasuwannin ƙasar.

Da take magana a shirin Politics Today na Channels TV ranar Alhamis, ministar ta ce ‘yan sumoga ne ke cutar da ‘yan ƙasa ta hanyar shigo da kayan da ba su da inganci.

“Kwarai da gaske akwai matsaloli kuma suna tasowa ne saboda fasa ƙwaurin kayayyaki zuwa cikin ƙasa,” in ji ta.

“Akwai ‘yan ƙasa marasa kishi da ke shigo da shinkafa maras inganci, wata ma bai kamata ɗan Adam ya ci ba, amma haka za su kawo ta kasuwa.”

Ministar ta jaddada cewa akwai rundunonin haɗin gwiwa da gwamnati ta samar don yaƙi da fasa ƙwauri “da kuma daƙile ayyukan masu kawo wa tattalin arzikin ƙasa cikas”.

Gwamnatin Najeriya ta haramta shigar da shinkafa ƙasar daga ƙasashen waje da zummar haɓaka nomanta a ƙasar.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...