Kungiyar RATTAWU ta aike da ta’aziyyar mutane 22 yan wasan Kano da suka rasu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Kungiyar ma’aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar Kano (RATTAWU) ta ce tana mika sakon ta’aziyya ga iyalai da yan uwan mutane 22 da suka yi hatsarin dake cikin tawagar wakilan jihar Kano a gasar wasanni ta Kasa a ka gudanar a jihar Ogun.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar reshen jihar Kano Comrade Babangida Mamuda Biyamusu ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Sanarwar ta baiyyana matasan a matsayin zakakurai kuma “yan kishin jihar kano wanda tarihin kano ba zai taba mantawa dasu ba.

Comrade Babangida Mamuda Biyamusu ya baiyyana cewa daukacin ‘ya’yan kungiyar ta RATTAWU sun nuna jimamin su da Babban rashin tare da addu’ar Allah ya gafar ta musu yasa aljannatul Firdausi ce makomar su ya kuma baiwa iyalan su hakurin jure Babban rashin ya kuma tashi kafadun wadanda suka jikkata.

InShot 20250309 102403344

Sanarwar ta aike da sakon ta’aziyya ga iyalan mamatan da gwamnan kano da Mai martaba sarkin kano da ma’aikatar matasa da wasanni dama al’umma jihar Kano baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...