Yan Sumoga ne ke Jawo Tashin Farashin Shinkafa a Niigeria – Ministar Kudi

Date:

Daga Maryam Adamu Mustapha

Ministar Kuɗi ta Najeriya Zainab Ahmed ta ce masu fasa ƙwauri ko kuma sumoga ne ke jawo tashin farashin shinkafa a kasuwannin ƙasar.

Da take magana a shirin Politics Today na Channels TV ranar Alhamis, ministar ta ce ‘yan sumoga ne ke cutar da ‘yan ƙasa ta hanyar shigo da kayan da ba su da inganci.

“Kwarai da gaske akwai matsaloli kuma suna tasowa ne saboda fasa ƙwaurin kayayyaki zuwa cikin ƙasa,” in ji ta.

“Akwai ‘yan ƙasa marasa kishi da ke shigo da shinkafa maras inganci, wata ma bai kamata ɗan Adam ya ci ba, amma haka za su kawo ta kasuwa.”

Ministar ta jaddada cewa akwai rundunonin haɗin gwiwa da gwamnati ta samar don yaƙi da fasa ƙwauri “da kuma daƙile ayyukan masu kawo wa tattalin arzikin ƙasa cikas”.

Gwamnatin Najeriya ta haramta shigar da shinkafa ƙasar daga ƙasashen waje da zummar haɓaka nomanta a ƙasar.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...