Yan Sumoga ne ke Jawo Tashin Farashin Shinkafa a Niigeria – Ministar Kudi

Date:

Daga Maryam Adamu Mustapha

Ministar Kuɗi ta Najeriya Zainab Ahmed ta ce masu fasa ƙwauri ko kuma sumoga ne ke jawo tashin farashin shinkafa a kasuwannin ƙasar.

Da take magana a shirin Politics Today na Channels TV ranar Alhamis, ministar ta ce ‘yan sumoga ne ke cutar da ‘yan ƙasa ta hanyar shigo da kayan da ba su da inganci.

“Kwarai da gaske akwai matsaloli kuma suna tasowa ne saboda fasa ƙwaurin kayayyaki zuwa cikin ƙasa,” in ji ta.

“Akwai ‘yan ƙasa marasa kishi da ke shigo da shinkafa maras inganci, wata ma bai kamata ɗan Adam ya ci ba, amma haka za su kawo ta kasuwa.”

Ministar ta jaddada cewa akwai rundunonin haɗin gwiwa da gwamnati ta samar don yaƙi da fasa ƙwauri “da kuma daƙile ayyukan masu kawo wa tattalin arzikin ƙasa cikas”.

Gwamnatin Najeriya ta haramta shigar da shinkafa ƙasar daga ƙasashen waje da zummar haɓaka nomanta a ƙasar.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...