Wasu Jami’an lafiya daga Sokkoto sun ziyarci Kano don Koyan aikin kula fa lafiya

Date:

Daga Kabiru Harun Yakasai

 

Darakta Janar na Hukumar Samar da Magunguna ta Jihar Kano, Pharmacist Hisham Imamuddeen ya karbi bakuncin rukunin wasu jami’ai daga ma’aikatar lafiya ta Jihar Sakkwato a rangadin binciken da suka kai hukumar a ranar Larabar data gabata.

Tawagar da ta kai ziyarar, ta kunshi manyan jami’an gudanarwa na ma’aikatar wanda ke karkashin jagorancin Pharmacist Murtala, da sauran masu ruwa da tsaki a sha’anin kula da lafiyar al’ummar jihar Sokoto.

Cikin wata sanarwa da jami’ar yada labarai ta ma’aikatar lafiya ta jihar kano Hadiza M Namadi ta aikowa kadaura24 tace Pharm. Hisham Imamudeen, a yayin da yake yi musu bayani kan ayyuka da kuma nasarorin da hukumar ta samu a baya-bayan nan, ya kuma yabawa Gwamna Abdullahi Umar Ganduje bisa yadda yake bayar da goyon baya ga fannin lafiya.

Ya bayyana matukar jin dadinsa da godiya ga Gwamna bisa yadda ya ware kaso mai tsoka ga fannin lafiya a cikin daftarin kasafin kudin shekarar 2022 da kuma tallafawa hanyoyin samar da kayayyaki duk da nufin inganta rayuwar al’ummar jihar kano.

Tun da farko a jawabin nasa, Shugaban Kungiyar, Pharm. Murtala ya ce sun zo Kano ne domin ganin irin aiyukan da hukumar take saboda su ma su yi koyi don su inganta hukumarsu tare da bunkasa lafiyar al’umma.

Daga nan Pharm. Murtala ya bayyana jin dadinsa da abin da suka gani, don haka ya yaba da aiyukan da aka suka gani da irin tarbar da aka yi musu,sannan ya yi alkawarin yin koyi da tsarin jihar Kano wajen inganta harkar samar da kayayyakin kula da lafiya a jiharsu.

Ya kuma godewa DG da daukacin ma’aikatan gudanarwar sa bisa karramawar da suka yi masu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...