Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

Date:

 

 

Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da gwamnatin Kano ke saki ya nuna cewa akwai gurɓatar iska a wasu unguwanni a cikin ƙwaryar Kano, inda hakan zai ƙara ta’azzara yaɗuwar cuttutuka a cikin al’umma.

Rahoton, wanda Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ta fitar bayan gwajin lafiyar iska da ta yi tsakanin 26 zuwa 30 ga watan Mayun da mu ka yi bankwana da shi, ya nuna cewa unguwanni kamar su Gaida, Ja’en, Sabon Titi da Sharada Kasuwa, basu da lafiyayyar iska, inda sakamakon ya nuna akwai gurɓatar iska a waɗannan unguwanni.

 

IMG 20250415 WA0003
Talla

 

Kwamishinan Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi, Dakta Dahir M Hashim ne ya wallafa rahoton a shafin sa na Facebook.

Rahoton ya nuna cewa gwamnatin Kano na shirin kai ɗauki a wadannan unguwanni sakamakon gurɓacewar iska, inda ta nuna damuwa kan karin gurɓacewar yanayi da ake samu a jihar.

InShot 20250309 102403344

Ya kuma nuna cewa kula da muhalli hakki ne na gaba daya al’umma ba wai gwamnati kaɗai ba.

Daily Nigerian

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...