Yanzu-yanzu:Kotu ta baiwa hukumar zaben Kano umarni Kan zaben kananan hukumomi

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja karkashin jagorancin mai Shari’a Emeka Nwite, ta bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar da ta dakata daga karbar Naira miliyan 10 ga masu takarar shugabannin kananan hukumomin da Naira miliyan 5 ga masu takarar kansilolin a zabe mai zuwa.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa a kwanakin baya, hukumar zaben ta sanya Naira miliyan 10 ga yan takarar kujerun ciyamomi da naira miliyan 5 ga masu takarar kujerun kansilolin a zaɓen da za’a a gudanar a watan gobe.

Yan arewa ku yi mana aikin gafara, mun gaza kare ku – ACF

Tun a wancan lokacin ne dai al’umma sukai ta kokawa game da kudin, amma hukumar ta ce ta sanya kuɗin da yawa ne saboda halin da tattalin arzikin kasa yake ciki.

Jam’iyyun SDP da APP da ADP ne dai suka shigar da karar, inda suka kalubalanci kudaden da hukumar KANSIEC ta sanya, sakamakon yawan da suka yi.

Barr. Hassan Tanko kyaure ne dai ya shigar da karar a madadin jam’iyyun guda uku, Kuma shi ne zai tsaya musu a gaban Kotun.

Iftila’i: Rushewar gini ta yi sanadiyar rasuwar mutane 2 a Kano

Kotun ta ce kada hukumar ta sake ta karɓi ko sisin kobo a hannun masu shiga takara har sai ta saurari kundarin Shari’ar.

Kotun dai ta sanya ranar 25 ga watan satumba na wannan shekarar a matsayin ranar da zata saurari kundarin Shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...