Yanzu-yanzu:Kotu ta baiwa hukumar zaben Kano umarni Kan zaben kananan hukumomi

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja karkashin jagorancin mai Shari’a Emeka Nwite, ta bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar da ta dakata daga karbar Naira miliyan 10 ga masu takarar shugabannin kananan hukumomin da Naira miliyan 5 ga masu takarar kansilolin a zabe mai zuwa.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa a kwanakin baya, hukumar zaben ta sanya Naira miliyan 10 ga yan takarar kujerun ciyamomi da naira miliyan 5 ga masu takarar kujerun kansilolin a zaɓen da za’a a gudanar a watan gobe.

Yan arewa ku yi mana aikin gafara, mun gaza kare ku – ACF

Tun a wancan lokacin ne dai al’umma sukai ta kokawa game da kudin, amma hukumar ta ce ta sanya kuɗin da yawa ne saboda halin da tattalin arzikin kasa yake ciki.

Jam’iyyun SDP da APP da ADP ne dai suka shigar da karar, inda suka kalubalanci kudaden da hukumar KANSIEC ta sanya, sakamakon yawan da suka yi.

Barr. Hassan Tanko kyaure ne dai ya shigar da karar a madadin jam’iyyun guda uku, Kuma shi ne zai tsaya musu a gaban Kotun.

Iftila’i: Rushewar gini ta yi sanadiyar rasuwar mutane 2 a Kano

Kotun ta ce kada hukumar ta sake ta karɓi ko sisin kobo a hannun masu shiga takara har sai ta saurari kundarin Shari’ar.

Kotun dai ta sanya ranar 25 ga watan satumba na wannan shekarar a matsayin ranar da zata saurari kundarin Shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...