Iftila’i: Rushewar gini ta yi sanadiyar rasuwar mutane 2 a Kano

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

An tabbatar da mutuwar mutum biyu, wasu biyu kuma sun tsallake rijiya da baya, a sakamakon rushewar wani bene mai hawa biyu a Jihar Kano.

Da misalin ƙarfe biyu a dare kafin wayewar garin ranar Alhamis ne benen ya rushe da su a unguwar Nomansland da ke Ƙaramar Hukumar Fagge.

Karin kudin mai: Gwamnan Legos ya sassautawa ma’aikatan jihar

Benen ya rushe ne a sakamakon ambaliyar ruwa, kasancewar yana kusa ne da hanyar ruwan.

Benen ya rushe ne a sakamakon ambaliyar da ta biyo bayan ruwan sama kamar da baƙin kwarya na tsawon sa’o’i a cikin daren.

Kotu ta tusa keyar alƙalin bogi zuwa gidan yari a Kano

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta sanar da hakan a safiyar Alhamis.

Kakakin hukumar, Samun Abdullahi, ya ce an garzaya da waɗanda aka ceto daga bene d ya rushe zuwa asibiti, inda suke samun kulawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...