Da dumi-dumi: Ogan Boye ya ajiye mukaminsa na Mai baiwa gwamnan Kano shawara Kan Matasa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Amb. Imam Yusuf wanda aka fi sani da Oga Boye ya Ajiye mukaminsa na mai baiwa gwamnan jihar kano shawara kan harkokin matasa.

Ogan Boye ya Mika takardar ajiye aikin nasa ne a Ofishin Sakataren gwamnatin jihar kano a wannan rana ta talata.

Za a shafe kwana uku ana ruwa marka-marka a wasu jihohin Najeriya

Imam Yusuf ya ajiye mukaminsa nasa ne domin ya tsayawa takarar shugabancin Karamar Hukumar Nassarawa a cikin jam’iyyar NNPP Kwankwasiyya.

Idan za’a iya tunawa dokar Zaɓe ce ta ce dole duk mai sha’awar tsayawa takarar wata kujerar sai ya ajiye duk wani Mukami da aka nada shi kwana 90 kafin zaben.

Badakalar magungunan Kano: Mun fara bincike kuma za mu gurfanar da duk mai hannu – Muhuyi Magaji

Hakan nuni da cewa Ogan Boye ya shiga cikin jerin wadanda suke takarar shugabancin Karamar hukumar Nasarawa a zaɓen da za’a gudanar a ranar 30 ga watan Nuwanba mai zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...