Wasu yara ‘yan gida daya sun rasa rayukansu sakamakon ginin da ya rufta akansu a lokacin da suke cikin ɗaki.
Ginin ya rufto ne sakamakon mamakon ruwan sama lokacin da yaran suke bacci.
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Kano ta tabbatar da mutuwar mutum goma sha takwas sakamakon ambaliyar ruwa a sassan jihar.
Mahaifin yaran ya ce bai jima da kwanciya ba sai ya ji ƙara bayan anyi wani ruwa mai ƙarfi.
Da dumi-dumi: Tinubu ya bayar da umarnin biyan tallafin man fetur – Rahoto
“Ƙarar da na ji ta girgiza ko ina sai na firgita na tashi, ina miƙe wa sai na ji ƙarar ƙaramar yarinyata tana hun wayyo Allah a danne ni,ina fitowa kawai sai naga bangon daƙin gaba ɗaya ya fadi a kansu.” in ji mahaifin.
“Duka yarana biyar ne a cikin daƙin daya rushe.”
Mahaifin ya ce moƙocin shi ne ya taimaka masa suka ɗaga wani katako inda suka samu suka fito da yara uku yayin da kuma aka kasa ceton sauran biyun.
Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa na jihar Kano,Isiyaku Abudllahi Kubarachi ya ce ambaliyar ruwa a Kano ta yi sanadin mutuwar mutane da dama da kuma rushewar gine-gine.
NNPC Ya Magantu Kan Wahalar Mai A Nigeria
“Waɗanda suka rasa rayukansu a wannan shekarar a ƙananan hukumominmu muna da kamar mutum 18 a yanzu inda waɗansu ɗakuna ne suka faɗa musu a ka, wasu kuma gonankinsu za su je kuma guraren da akwai ruwa kuma za su tsallaka, daga nan ne ake samun matsala.” in ji shugaban.
Shugaban ya kuma ce a cikin ƙiyasinsu gabakiɗaya dai akwai mutum 8,773 waɗanda irin wannan lamarin ya shafa a jihar Kano.
BBC Hausa