Rundunar yan sanda ta magantu kan kisan masu zanga-zangar yunwa a Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kano, Salman-Dogo Garba, ya ce rundunar ba ta da labarin asarar rai a lokacin zanga-zangar yunwa da tsadar rayuwa da aka gudanar.

Kwamishinan ya bayyana haka ne ranar Litinin a lokacin ganawarsa da ’yan jarida, inda ya ce rundunar ta kama mutane 873 kan laifin lalatawa da sace dukiyoyin jama’a da na gwamnati a lokacin zanga-zangar.

“A iya bayanan da muke da su, zuwa yanzu ba mu da rahoton asarar rai a yayin zanga-zangar,” in ji shi.

Dan Bello ya sanya wa jam’iyyar APCn Kano sharadin dakatar da yi mata bankade-bankade

Idan za a iya tunawa Daily trust ta kawo rahoton iyalan wasu matasa akalla uku da aka kashe a lokacin zanga-zangar, ciki har da wata budurwa da ake shirin daura aurenta.

Yan uwan wadanda aka kashe din, sun kuma yi zargin yan uwannasu sun rasu ne a sakamkon harbi daga jami’an tsaro, musamman ’yan sanda.

Iyalan wadanda suka rasun dai sun bayyana damuwa bisa yadda zanga-zangar da aka shirya ta lumana ta yi ajalinsu, inda suka bukaci a bi musu hakkinsu.

Zanga-zangar lumanar ta rikide zuwa tarzoma ne bayan da bata-gari suka kwace ta, suka rika fasa wurare suna sace-sace, tare da jikkata mutane a sassan jihar.

Yadda aka sace Naira biliyan 50 daga asusun Gwamnatin Kano

An yi dauki ba dadi tsakanin bata-garin da jami’an tsaro a kofar gidan gwamnatin jihar da sauran sassan jihar, inda aka kama sama da mutum 100.

Kazancewar lamarin ya kai ga gwamnatinn jihar, Abba Kabir, sanya dokar hana fita tsawon awa 24, kafin daga bisani a sassauta dokar.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...