Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kano ta dage dokar hana fita

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnatin jihar kano ta sanar da dage dokar hana fita da ta sanya sakamakon yadda zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa ta rikide zuwa tashin hankali.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa gwamnatin jihar kano ta sanya dokar ne tun a ranar Alhamis ranar farko kenan da fara Zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa bayan wasu bata gari sun fake da zanga-zangar su ka rika fasawa da sace kayan gwamnati da na al’umma.

Dan Bello ya sanya wa jam’iyyar APCn Kano sharadin dakatar da yi mata bankade-bankade

Kwamishinan yada labarai na jihar kano Baba Halilu Dantiye ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai a Kano.

Yace gwamnatin ta dauki wannan matakinne sakamakon yadda al’amura suka koma daidai, zaman lafiya ya dawo jihar yadda ya dace.

Hakan dai yana nufi an dage dokar kwata-kwata a kwanaki masu zuwa, mutane za su iya cigaba da harkokinsu na yau da kullum.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...