Rundunar yan sanda ta magantu kan kisan masu zanga-zangar yunwa a Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kano, Salman-Dogo Garba, ya ce rundunar ba ta da labarin asarar rai a lokacin zanga-zangar yunwa da tsadar rayuwa da aka gudanar.

Kwamishinan ya bayyana haka ne ranar Litinin a lokacin ganawarsa da ’yan jarida, inda ya ce rundunar ta kama mutane 873 kan laifin lalatawa da sace dukiyoyin jama’a da na gwamnati a lokacin zanga-zangar.

“A iya bayanan da muke da su, zuwa yanzu ba mu da rahoton asarar rai a yayin zanga-zangar,” in ji shi.

Dan Bello ya sanya wa jam’iyyar APCn Kano sharadin dakatar da yi mata bankade-bankade

Idan za a iya tunawa Daily trust ta kawo rahoton iyalan wasu matasa akalla uku da aka kashe a lokacin zanga-zangar, ciki har da wata budurwa da ake shirin daura aurenta.

Yan uwan wadanda aka kashe din, sun kuma yi zargin yan uwannasu sun rasu ne a sakamkon harbi daga jami’an tsaro, musamman ’yan sanda.

Iyalan wadanda suka rasun dai sun bayyana damuwa bisa yadda zanga-zangar da aka shirya ta lumana ta yi ajalinsu, inda suka bukaci a bi musu hakkinsu.

Zanga-zangar lumanar ta rikide zuwa tarzoma ne bayan da bata-gari suka kwace ta, suka rika fasa wurare suna sace-sace, tare da jikkata mutane a sassan jihar.

Yadda aka sace Naira biliyan 50 daga asusun Gwamnatin Kano

An yi dauki ba dadi tsakanin bata-garin da jami’an tsaro a kofar gidan gwamnatin jihar da sauran sassan jihar, inda aka kama sama da mutum 100.

Kazancewar lamarin ya kai ga gwamnatinn jihar, Abba Kabir, sanya dokar hana fita tsawon awa 24, kafin daga bisani a sassauta dokar.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...