Atiku ya gargadi hafsoshin tsaron Nigeria kan harbin masu zanga-zanga

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya gargadi hafsoshin tsaron Nigeria da kwamandojin soji a kan ba da izinin amfani da muggan makamai a kan masu zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a fadin Nigeria .

A wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Talata, Atiku ya ce za a daurawa shugabannin tsaro alhakin harbin fararen hula masu zanga-zangar lumana da sojoji da sauran jami’an tsaro suke yi.

Talla
Talla

Ya rubuta: “Ina so in yi tsattsauran gargaɗi ga manyan hafsoshin tsaro da kwamandojin sojan Najeriya, musamman waɗanda suke ba da izinin yin amfani da bindiga wajen harbin masu zanga-zangar lumana, su sani cewa su za a tuhuma da aikata laifuffukan cin zarafin bil adama, ko da bayan sun yi ritaya daga aiki.”

Bayan koken al’ummar Kano, shugabannin Singa sun ce yan kasuwar su ji tsoron Allah

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya yi kira ga hukumomin tsaron da su tabbatar da baiwa masu zanga-zangar kariya, domin abun da suke yi dokar kasa ce ta ba su damar yi.

“Hakkin da ya rataya a wuyan gwamnati da hukumomin tsaro ne su tabbatar da tsaro da kariya ga mutanen da ke su ka yar da zasu nemi ‘yancinsu ta hanyar gudanar da zanga-zangar lumana.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...