Daga Rahama Umar Kwaru
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya gargadi hafsoshin tsaron Nigeria da kwamandojin soji a kan ba da izinin amfani da muggan makamai a kan masu zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a fadin Nigeria .
A wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Talata, Atiku ya ce za a daurawa shugabannin tsaro alhakin harbin fararen hula masu zanga-zangar lumana da sojoji da sauran jami’an tsaro suke yi.
Ya rubuta: “Ina so in yi tsattsauran gargaɗi ga manyan hafsoshin tsaro da kwamandojin sojan Najeriya, musamman waɗanda suke ba da izinin yin amfani da bindiga wajen harbin masu zanga-zangar lumana, su sani cewa su za a tuhuma da aikata laifuffukan cin zarafin bil adama, ko da bayan sun yi ritaya daga aiki.”
Bayan koken al’ummar Kano, shugabannin Singa sun ce yan kasuwar su ji tsoron Allah
Tsohon mataimakin shugaban kasar ya yi kira ga hukumomin tsaron da su tabbatar da baiwa masu zanga-zangar kariya, domin abun da suke yi dokar kasa ce ta ba su damar yi.
“Hakkin da ya rataya a wuyan gwamnati da hukumomin tsaro ne su tabbatar da tsaro da kariya ga mutanen da ke su ka yar da zasu nemi ‘yancinsu ta hanyar gudanar da zanga-zangar lumana.”