Atiku ya gargadi hafsoshin tsaron Nigeria kan harbin masu zanga-zanga

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya gargadi hafsoshin tsaron Nigeria da kwamandojin soji a kan ba da izinin amfani da muggan makamai a kan masu zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a fadin Nigeria .

A wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Talata, Atiku ya ce za a daurawa shugabannin tsaro alhakin harbin fararen hula masu zanga-zangar lumana da sojoji da sauran jami’an tsaro suke yi.

Talla
Talla

Ya rubuta: “Ina so in yi tsattsauran gargaɗi ga manyan hafsoshin tsaro da kwamandojin sojan Najeriya, musamman waɗanda suke ba da izinin yin amfani da bindiga wajen harbin masu zanga-zangar lumana, su sani cewa su za a tuhuma da aikata laifuffukan cin zarafin bil adama, ko da bayan sun yi ritaya daga aiki.”

Bayan koken al’ummar Kano, shugabannin Singa sun ce yan kasuwar su ji tsoron Allah

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya yi kira ga hukumomin tsaron da su tabbatar da baiwa masu zanga-zangar kariya, domin abun da suke yi dokar kasa ce ta ba su damar yi.

“Hakkin da ya rataya a wuyan gwamnati da hukumomin tsaro ne su tabbatar da tsaro da kariya ga mutanen da ke su ka yar da zasu nemi ‘yancinsu ta hanyar gudanar da zanga-zangar lumana.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...