Tinubu na bibiyar yadda zanga-zanga ke gudana a Nigeria – Minista

Date:

Shugaban kasa Bola Tinubu na kallon yadda zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa ke gudana a fadin Nigeria.

Ministan Kasafin Kudi da Tsare Tattalin Arziki, Atiku Bagudu ne ya bayyana hakan yayin wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin din channels .

Zanga-zangar da aka yi a Najeriya a baya-bayan nan na da nasaba da tsadar rayuwa, da tabarbarewar farashin Naira da kuma cire tallafin man fetur da gwamnatin Tinubu ta yi.

Talla
Talla

Ko da yake an yi ta kiraye-kirayen ga Tinubu ya yi jawabi ga al’ummar kasar bayan zanga-zangar ta shiga kwana na uku, amma har yanzu shugaba Tinubu bai yi hakan ba.

Sai dai Bagudu, ya ce shugaban na Najeriya ya san halin da ake ciki sosai.

“Shugaban kasa ya na sane da halin da ake ciki, yadda ya kamata .”in ji Ministan

Yadda Jaruma Rahama Sadau ta raba Naira Miliyan 1 ga Masoyanta

”Ni minista ne. Akwai nauyi akai na. Ni ma ina bibiyar halin da ake ciki saboda na sami abun da zan ce game da bayanan da zan shigar.”

Bagudu ya ce “Mu na ji kuma mu na kallon abun da ke faruwa game da zanga-zangar.”

Dan Iliyasu Satame da al’ummar Obajana za su shiryawa Ɗangote saukar alqur’ani 10

Ministan wanda ya amince da cewa ana shan wahala a Najeriya, amma gwamnatin tarayya na kokarin ganin an samu saukin rayuwa ga ‘yan kasar.

“Duk duniya ana fuskantar matsalar tsadar rayuwa rayuwa, amma za mu saurara kuma muna kuma daraja abubuwan da ‘yan Najeriya ke fada”.

Solacebase

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...