Gwamnatin tarayya ta bayyana dalilin da yasa ba za ta sanar da wuraren sayar da shinkafar dubu 40 ba

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Ministan yada labarai da wayar da kan al’umma na kasa, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin tarayya ba za ta bayyana wuraren da zata sayar da Shinkafar da ta karyar da farashin ta zuwa Naira dubu 40 ba, saboda gudun ka da masu kudi su je su saye.

Ministan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake amsa tambayoyin manema ranar laraba a Abuja.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa Gwamnatin Tarayya ta bakin Ministan a ranar Litinin, ta ce ta samar da cibiyoyi a fadin kasar nan inda ‘yan Najeriya za su iya siyan buhunan shinkafa 50kg a kan Naira 40,000.

Talla
Talla

Idris ya ce wannan shiri na daya daga cikin tsare-tsaren da gwamnatin Tinubu ta fito da su domin saukakawa yan kasa tsadar rayuwa.

Sai dai da yake magana a ranar Larabar da ta gabata, ministan ya ce ana shirin raba buhunhunan shinkafar zuwa jihohin Nigeria.

Karin bayani kan jadawalin zaɓen kananan hukumomi na Kano

Ya kara da cewa, ba za a iya bayyana wuraren da za a sayar da su a fadin kasar nan ba saboda dalilai na tsaro, kuma don tabbatar da cewa talakawa da akai tsarin don su sun sami shinkafar.

“Zai yj wahala a ambaci wuraren da za a sayar da Shinkafar saboda dalilan tsaro.

Talla

“Amma muna da shinkafar a kasa, kuma za a sayar da ita a kan N40,000.

“An riga an samu shinkafar, zan iya tabbatar da cewa za a sayar da ita a wurare daban-daban a fadin kasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...