Da dumi-dumi: Tinubu ya rage farashin Shinkafa a Nigeria

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnatin Najeriya ta ce ta rage farashin buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50 da kashi 50 zuwa N40,000 a fadin kasar.

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa Mohammed Idris ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a karshen taron majalisar zartarwa ta tarayya da aka yi ranar Litinin a Abuja.

Talla
Talla

A cewarsa, rage farashin shinkafar ya zo ne a daidai lokacin da aka tura motocin dakon kaya 20 ga gwamnonin jihohi daban-daban domin rabawa ‘yan Najeriya.

Za mu duba tare da bayar da magunguna kyauta ga marasa lafiya a karamar hukumar Wudil – Bilkisu Indabo

Ya ce sun kuma rage farashin Shinkafar da kusan kashi 50 na kudinta ga yan Nigeria, tuni an tura Shinkafar wurare daban-daban a jihohin kasar nan domin sayar da ita akan farashin naira dubu 40. An samar da cibiyoyi, ta yadda masu bukatar wannan shinkafa za su je can su saya a kan Naira 40,000,” inji shi.

A halin da ake ciki kuma, wani binciken da kadaura24 ta gudanar ya nuna cewa ana sayar da buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50 tsakanin N75,000 zuwa N80,000 a wasu daga cikin Kasuwannin Kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Amfani da al’ada a cikin fina-finan kannywood ne ya hana masa’antar ci gaba – Khadija Osi

Jaruma a masana'antar Kannywood Khadija Muhammad wacce aka fi...

Nasarar da Ɗaliban Kano suka Samu a NECO Kokari ne na Gwamnatin Ganduje – Sanusi Kiru

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Hon. Muhammad Sanusi...

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano

Kwana biyu bayan rikicin wutar lantarki tsakanin Asibitin Koyarwa...

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar...