Da dumi-dumi: Tinubu ya rage farashin Shinkafa a Nigeria

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnatin Najeriya ta ce ta rage farashin buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50 da kashi 50 zuwa N40,000 a fadin kasar.

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa Mohammed Idris ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a karshen taron majalisar zartarwa ta tarayya da aka yi ranar Litinin a Abuja.

Talla
Talla

A cewarsa, rage farashin shinkafar ya zo ne a daidai lokacin da aka tura motocin dakon kaya 20 ga gwamnonin jihohi daban-daban domin rabawa ‘yan Najeriya.

Za mu duba tare da bayar da magunguna kyauta ga marasa lafiya a karamar hukumar Wudil – Bilkisu Indabo

Ya ce sun kuma rage farashin Shinkafar da kusan kashi 50 na kudinta ga yan Nigeria, tuni an tura Shinkafar wurare daban-daban a jihohin kasar nan domin sayar da ita akan farashin naira dubu 40. An samar da cibiyoyi, ta yadda masu bukatar wannan shinkafa za su je can su saya a kan Naira 40,000,” inji shi.

A halin da ake ciki kuma, wani binciken da kadaura24 ta gudanar ya nuna cewa ana sayar da buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50 tsakanin N75,000 zuwa N80,000 a wasu daga cikin Kasuwannin Kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...