Za mu duba tare da bayar da magunguna kyauta ga marasa lafiya a karamar hukumar Wudil – Bilkisu Indabo

Date:

Daga Samira Ahmad

 

Shugabar riko ta karamar hukumar wudil Hajiya Bilkisu Yakubu Indabo ta ce zata hada gwiwa da hukumar masu yiwa kasa hidima wajen ba da magunguna kyauta da al’ummar karamar hukumar.

“Cikin wata yarjejeniyar haɗin gwuiwa da mukayi tsakanin Ƙaramar Hukumar Wudil da reshen ɗalibai masu bautawa ƙasa (NYSC) na Wudil, zamu gudanar da wata shirin dubawa da rabon magungunnan cututtuka irin su hawan jini, zazzaɓin typhoid da shauran nau’ikan gama garin cututtuka”.

Talla
Talla

Hajiya Bilkisu Indabo ta bayyana hakan ne yayin wata ganawa da jaridar kadaura24.

“In sha Allahu nan da ƴan kwanaki kaɗan zamu sanar da ranar da zamu gudanar da wannan taro domin al’ummar Ƙaramar Hukumar Wudil su fito su amfana”. Inji Shugabar

Rarara ya Magantu AKan Goge Shafinsa da Facebook Ya Yi

Ta ce da ma bannin kula da lafiyar al’umma na daga cikin manyan abubunwan da ta fi baiwa muhimmanci, ta kuma yi alkawarin cigaba da Kula da lafiya da Ilimi a karamar hukumar .

“Kamar yadda aka sani, a matsayi na ta ma’aikaciyar lafiya kuma malamar ilimi, zan cigaba da bayarda da fifiko a wannan ɓangare dama shauran ɓangarori masu amfani kai tsaye ga al’umma ta domin bauta musu yadda ya dace”. A cewar Bilkisu Indabo

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...