Iftila’i: Gobara ta hallaka ‘yar Kwamishina a Kano, da yan uwansa biyu

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

Gobara ta yi sanadiyar hallaka yar Kwamishinan ilimi mai zurfi na jihar Kano, Yusuf Kofar-Mata, tare da wasu yan uwansa guda biyu.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne a shafin sa na Facebook a ranar Laraba.

Marigayiyar dai ‘yarsa ce mai suna Maimuna, sai yayarsa, Khadija, da matar dan uwansa, Juwairiyya.

Talla

Rahotanni sun bayyana cewa gobara ta kone gidan kwamishinan da ke Kofar-Mata a birnin Kano da safiyar Laraba yayin da iyalan ke barci.

Wata majiyar daga cikin danginsa ta ce gobarar ta lalata wasu kayayyaki masu daraja a gidan.

Musa Iliyasu Kwankwaso ya soki gwamnatin Kano kan sabbin masarautu masu daraja ta biyu

Kakakin hukumar kashe gobara ta jihar, Abdullahi Saminu, ya ce har ba a iya gano adadin barnar da gobarar ta yi ba, da kuma musabbabin tashin gobarar.

A halin da ake ciki, Kofar-Mata ya bayyana alhininsa game da rasuwar yar tasa da wasu ’yan uwansa guda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu:yanzu: Gwamnan kano ya yi sabbin nade-naden mukamai

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Gwamann jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Daga Fatima Mahmoud Diso   Shugabanni da jagororin jam'iyyar APC na...