Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Date:

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar Dattijai da ta dawo da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, wadda aka dakatar.

Yayin yanke hukunci, Mai Shari’a Binta Nyako ta bayyana cewa dakatar da Natasha na tsawon watanni shida ya yi tsauri fiye da kima.

InShot 20250309 102512486
Talla

Kotun ta ce Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, bai yi kuskure ba lokacin da ya hana Natasha magana a zauren majalisa, saboda a lokacin ba ta zaune kan kujerar da aka ware mata ba. Sai dai kotun ta bukaci Natasha ta bai wa majalisar hakuri.

A cewar kotun, tun da majalisa tana da kwanaki 181 a kowanne zango, dakatar da Natasha tsawon watanni shida ya yi kama da hana mazaɓarta wakilci har na kusan kwanaki 180.

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Kotun ta jaddada cewa duk da cewa majalisar na da ikon ladabtar da ɗan majalisa, bai kamata hukuncin ya kai ga hana ayyukan wakilci ba.
Mai shari’a Nyako ta kuma yi watsi da ƙarar Akpabio na cewa kotun ba ta da hurumin sauraron shari’ar.

Majalisar Dattawa ta dakatar da Natasha a watan Maris bayan ta zargi Shugaban Majalisar, Sanata Godswill Akpabio, da cin zarafi ta fuskar lalata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...