Gwamnan Kano ya Nada Mai rikon Mukamin Manajan Daraktan ARTV

Date:

Daga Mubina Mahmoud

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin Hajiya Hauwa Isa Ibrahim a matsayin mai rikon mukamin Manajan Darakta ta gidan talabijin na Abubakar Rimi (ARTV).

Kadaura24 ta rawaito cewa nadin ya biyo bayan dakatarwar da aka yi wa manajan darakta Mustapha Indabawa.

Dakatarwar ta zo ne bayan jerin rahotannin da jaridar kadaura24 ta rika yi kan zarge-zarge da Ake yi masa, wanda hakan ya jawo hankalin hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta kano ta gudanar da bincike, inda daga karshe ta baiwa gwamnan Kano shawarar a dakatar da shi .

Gaskiyar Lamari Kan Halin Da Ake Ciki a Masarautar Kano

Wasikar nadin mai kwanan wata 27 ga Mayu 2024 ta samu sa hannun Abdullahi Baffa Bichi, sakataren gwamnatin jihar.

Wasikar ta umurce ta da ta karbi harkokin gidan talabijin din nan take.

Kafin nadin nata, Hajiya Hauwa Isa Ibrahim ita ce mataimakiyar Manajan Daraktan gidan talabijin din na ARTV.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...