Gwamnan Kano ya Nada Mai rikon Mukamin Manajan Daraktan ARTV

Date:

Daga Mubina Mahmoud

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin Hajiya Hauwa Isa Ibrahim a matsayin mai rikon mukamin Manajan Darakta ta gidan talabijin na Abubakar Rimi (ARTV).

Kadaura24 ta rawaito cewa nadin ya biyo bayan dakatarwar da aka yi wa manajan darakta Mustapha Indabawa.

Dakatarwar ta zo ne bayan jerin rahotannin da jaridar kadaura24 ta rika yi kan zarge-zarge da Ake yi masa, wanda hakan ya jawo hankalin hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta kano ta gudanar da bincike, inda daga karshe ta baiwa gwamnan Kano shawarar a dakatar da shi .

Gaskiyar Lamari Kan Halin Da Ake Ciki a Masarautar Kano

Wasikar nadin mai kwanan wata 27 ga Mayu 2024 ta samu sa hannun Abdullahi Baffa Bichi, sakataren gwamnatin jihar.

Wasikar ta umurce ta da ta karbi harkokin gidan talabijin din nan take.

Kafin nadin nata, Hajiya Hauwa Isa Ibrahim ita ce mataimakiyar Manajan Daraktan gidan talabijin din na ARTV.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...