Yanzu-Yanzu: Malamai a Kano sun cire Sheikh Ibrahim Khalil Daga Shugabancin Majalisar Malamai

Date:

Daga Halima M Abubakar

 

Gamayyar kungiyoyin Malaman jihar Kano sun bayyana Cewa sun tsige Shugaban Majalisar Malaman ta Kano Sheikh Ibrahim Khalil Daga Shugabancin Majalisar bisa Wasu laufuka da suke tuhumar shehun Malamin.

 

Cikin Wata sanarwa da Ustaz Saifullahi Adam Assudani da Sheikh Khalifa Gama da sheikh Abdulkadir Ramadan da Kuma Imam Jamil Abubakar suka Sanyawa Hannu sun ce sun dauki Wannan Matakin ne da yawun dukkanin Malaman jihar Kano.
Sanarwar tace malam Ibrahim Khalil ya Gaza ciyar da Majalisar gaba,Sannan Suka ce Majalisar Bata aikin da aka dora Mata na yin Fatawa ga al’umma Kan sabbin Matsalolin da suke bijirowa a Wannan zamanin.
Suka ce yana Amfani da ofishin Majalisar Wajen taroka na kashin Kansa ba na Majalisar ba,  ya Gaza Kade Kan bangarorin Izala Qadirriyya da Tijjaniya a Kano Sannan Kuma Suka ce ya shiga Siyasa harma takara yake nema.
Sanarwar yace bisa Wadancan dalilai ne yasa dukkanin malamai daga bangaren Tijjaniya, Qadirriyya da Izala duka ga dacewar su sauke shi daga Shugabancin Majalisar, sai dai sun ce garanbawul din da aka yiwa Majalisar Shugaban Kadai ta shafa sauran Shugabanin Suna nan akan mukamansu.
Daga Karshe Sanarwar ta bayyana Cewa sun zabi Farfesa Abdullah Saleh Pakistan a Matsayin Sabon Shugaban Majalisar Malaman jihar Kano Kuma sun ce kowa daga kowanne bangare na Tijjaniya, Qadirriyya da Izala sun Amince da Wannan Mataki.

5 COMMENTS

  1. Allah ya kyauta, shikuma sabon Jagoran Allah yada fa masa ya kuma Hadekan musulmi baki daya, ya ye mana wannan masifun da muke fama dasu afadin Duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...