Gwamna Ganduje ya aike da ta’aziyyar rasuwar Muhammad Aminu Adamu (Abba Boss)

Date:

Daga Abubakar Yakubu Abubakar
 Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya koka kan rasuwar Alhaji Muhammad Aminu Adamu wanda aka fi sani da Abba Boss.
 Cikin Wata sanarwa da Abba Anwar Mai Magana da yawun Gwamnan ya aikowa Kadaura24 yace Gwamna Ganduje ya bayyana marigayin a matsayin fitaccen shugaba na gari, uba na ainihi ga mutane da yawa da suka zauna tare da shi, mai tarbiyya kuma ɗan tarbiyya, wanda ya yi imani da hidimtawa Rayuwar al’ummar .
 Ya kara da cewa, “Wannan mutuwa, ta zo ne lokacin da muke matukar bukatar sa, Saboda Mutum ne Mai karamci.
 Gwamna Ganduje ya ba da tabbacin cewa, marigayi Abba Boss, ɗan Najeriya ne mai kishin ƙasa, wanda ya damu ƙwarai da ci gaban al’ummarsa, jiharsa da ma ƙasa baki ɗaya.
 Ya kara da cewa, “babu shakka ya rasu yayin da muke bukatarsa, amma Allah Madaukakin Sarki ya fi son shshi muna addu’ar Allah yasa  kyawawan ayyukan su bishi”.
 “Don haka a madadin gwamnati da mutanen jihar Kano, ina mika ta’aziyyar mu ga iyalan Alhaji Muhammad Aminu Adamu, makusantan sa, abokan sa, masu son sa da sauran al’umma baki daya. Allah Ya gafarta masa dukkan kurakuran sa.  kuma ya saka masa da kyawawan ayyukansa da Jannatul Fiddaus, ”in ji gwamna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...