Gwamnan Kano ya Turawa Majalisar Dokoki Sunayen Kantomomi 44 Domin Tantancewa

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Gwamna Abba Kabir-Yusuf na jihar Kano ya mika sunayen shugabannin riko na kananan hukumomin jihar ga majalisar dokokin jihar ta domin tantance su.

Wannan na zuwa ne makonni uku, bayan karewar wa’adin zababbun shugabannin kananan hukumomin jihar.

Kakakin majalisar, Ismail Falgore, ne ya bayyana hakan a ranar Talata a zauren majalisar yayin da yake karanta takardar bukatar da gwamnan ya turawa majalisar.

Gwamna Abba Kabir Ya Mikawa Majalisar Kano Sunayen Kwamishinonin Da Zai Nada

Yayin da yake gabatar da sakon, shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Hussaini (NNPP-Dala), ya ce bukatar gwamnan ta biyo bayan karewar wa’adin zababbun shugabannin kananan hukumomin da mataimakansu ne tun a ranar 12 ga watan Fabrairu, 2023.

A cewarsa, jerin sunayen sun kunshi shugaba da mataimakinsa da sakatare na kowace karamar hukuma cikin kananan hukumomi 44 da ake da su a jihar.

Bidiyon Dala: Kotu ta Yanke Hukunci Kan Karar da Ganduje Ya Kai Hukumar Yaki da Cin Hanci ta Kano

Shugaban masu rinjaye ya bayyana cewa sashe na 58 na dokar kananan hukumomi ya bayyana cewa, idan wa’adin shugabancin kananan hukumomin jihar ya kare ya zama wajibi a gudanar da zabe.

Dokar ta kuma bayyana cewa gwamna na iya nada shuwagabannin riko da za su rika kula da harkokin majalisun kananan hukumomin na tsawon watanni uku.

Bayan tattaunawa, majalisar ta amince da kudurin, tare da kafa kwamitin wucin gadi da zai tantance wadanda aka nada a ranar Laraba 6 ga watan Maris.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...