Bidiyon Dala: Kotu ta Yanke Hukunci Kan Karar da Ganduje Ya Kai Hukumar Yaki da Cin Hanci ta Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta yanke hukuncin cewa hukumar karbar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ba ta da hurumin gudanar da bincike kan zargin karbar cin hanci da akewa tsohon gwamna Abdullahi Ganduje a wani bidiyon.

Majiyar kadaura24 ta Solacebase ta ruwaito cewa alkalin kotun, Mai shari’a Abdullahi Muhammad Liman a ranar Talata ya yanke hukuncin cewa laifin yana karkashin dokar tarayya da hukumar jihar ba ta da iko a kai.

Gwamna Abba Kabir Ya Mikawa Majalisar Kano Sunayen Kwamishinonin Da Zai Nada

Idan dai za a iya tunawa, Abdullahi Ganduje, tsohon gwamnan jihar Kano ya maka hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano a gaban kotu inda ya bukaci alkalai da su dakatar da binciken bidiyon dala da hukumar ta ce zata yi masa.

Sai dai Lauyan wanda ake kara na farko a karar, Hukumar Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano Barr. Usman Umar Fari ya ce za su daukaka kara kan hukuncin kotun.

Karin Bayani na nan tafe

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...